Wednesday, January 2, 2019

ANTSIGE MATAIMAKAN SHUWAGABANNIN KANANAN HUKUMOMI MULKI UKU A JIHAR ZAMFARA.

A yau ne wa'adin kananan hukumomi a jihar zamfara yake cika,  wanda aka masu na shekara uku kamar yadda doka ta tanada a jihar ya zamfara. Amma sai dai rashin samun aiwatar da zabe da ba'ayiba saboda dalilai na tsaro ya tilasta gwamnatin jihar neman majalisar dokokin jihar da ta  kara wa'adin wata uku ga shuwagabannin kananan hukumomin da kansilolan su.
Sai dai adai waje kuwa, majalisar dokokin jihar ta zamfara karkashin jagoranci Hon. Sanusi Garba Rikiji ta Ayyana wasu mataimakan kananan hukumomi guda uku wadanda Karin bai Shafa ba,  saboda basu biyayya ga gwamnatin Gwamna Abdul'aziz Yari.
Adai waje kuwa shima shugaban karamar hukumar Bukkuyum ya kwatanta irin wannan yunkuri ga wasu kansilolan Bukkuyum guda Hudu, inda yake tabbatar masu koda majalisar ta Kara wa'adin to sukam su San inda dare yamasu, don bazaiyi tafiya da suba tunda bakison gwamnatin Gwamna Abdul'aziz Yari Abubakar.

Daga

Aliyu Ahmad Gusau. 

No comments:

Post a Comment

GWAMNAN JIHAR ZAMFARA YA NISANTAR DA KANSA AKAN DAKATAR DA 'YAN MAJALISU HUDU DA AKAYI.

Daga Salisu Bello . Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya nisantar da kan sa da sa hannu wajen dakatar da 'yan Majalisar do...