Thursday, January 10, 2019

GWAMNAN JIHAR ZAMFARA YA NISANTAR DA KANSA AKAN DAKATAR DA 'YAN MAJALISU HUDU DA AKAYI.

Daga Salisu Bello .

Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya nisantar da kan sa da sa hannu wajen dakatar da 'yan Majalisar dokokin Jihar Zamfara guda hudu da Majalisar tayi karkashin jagorancin Rt Hon Sanusi Garba Rikiji a satin da ya gabata.

Wannan ya biyo bayan ganawar sirri da yayi tare da Sanata mai wakiltar Zamfara ta yamma kuma Babban jigo a siyasar Zamfara wato Sanata Ahmad Sani Yarima a gidanshi dake Abuja.

Gwamnan ya kuma bukaci Sanata Yarima da ya kira wadannan 'yan Majalisu domin basu hakuri  akan abunda ya faru wanda anyi shi ne ba bisa ka ka'ida ko doka ba.

Rahotannin da muke samu a yau sun nuna wadannan 'yan Majalisun suna Babban Birnin tarayya wato Abuja domin ganawar sirri da shi Sanata Ahmad Sani Yarima.

No comments:

Post a Comment

GWAMNAN JIHAR ZAMFARA YA NISANTAR DA KANSA AKAN DAKATAR DA 'YAN MAJALISU HUDU DA AKAYI.

Daga Salisu Bello . Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya nisantar da kan sa da sa hannu wajen dakatar da 'yan Majalisar do...