Wednesday, January 2, 2019

GWAMNATIN YARI BAZATA IYA GUDANAR DA ZABEN KANANAN HUKUMOMI BA.


Majalisar Dokokin a Zamfara ta kara waadain Shugabannin Kanan hukumomi 14, inda ta Tsige mataimakan Shugabannin 4 daga Mulki
-----------
Majalisar dokokin jahar Zamfara, yau laraba ta kara wa'adin Shugabannin kananan hukumomi goma sha hudu na jahar Zamfara, Wanda wa'adinsu ke karewa Yau 2 January 2019, wanda suka cika wa'adinsu na Shekara Ukku Kamar Yadda doka tayi tanadi. 

Majalisar takara masu wa'adi har zuwa ranar 2 April 2018, Haka kuma Majalisar dokokin ta Tsige wasu Shugabannin kanan hukumomi Ukku daga mukamansu wadanda suka hada da Mataimakan Shugabannin kananan hukumomin Zurmi, Birnin Magaji dana Gummi. 

Kamfanin dillacin Labaru na NAN, ya ruiwato cewa karin wa'adin ya biyo bayan rokonda Gwamnatin jahar Zamfara ta gabatar ga majalisa na neman a amince da karin wa'adin wanda kuma shugaban Majalisar Sanunsi Rikiji ya tabbatarda Karin waddin har nawata ukku wanda yace doka ta kananan hukumomi sakin layi na 15 karamin layi na hudu yabada damar karin waadin. 

Saidai wani danmajlisa mai wakiltar Maru ta Kudu, Hon. Abdullahi Muhammad Dansadau ya kalubalaci matakin tsige mataimakan shugabannin.

No comments:

Post a Comment

GWAMNAN JIHAR ZAMFARA YA NISANTAR DA KANSA AKAN DAKATAR DA 'YAN MAJALISU HUDU DA AKAYI.

Daga Salisu Bello . Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya nisantar da kan sa da sa hannu wajen dakatar da 'yan Majalisar do...