Hantsi Online news: Jarida ce da ke wallafa labaranta a shafin sada zumunta, wanda suka shafi, siyasa, Noma da Kiyo, addini, zamantakewa, kimiyyah, wasanni, adabi, kiwon lafiya, ra'ayoyi, martani, labarai da dumi-duminsa, d/s : jaridarhantsi@gmail.com
Thursday, January 3, 2019
MAJALISAR DOKOKIN JIHAR ZAMFARA TA DAKATAR DA YAN MAJALISU GUDA HUDU (4) KAN GOYON BAYAN G8 DA SUKAI.
Daga Bello Ahmad Tsafe...
Majalisar dokokin jihar Zamfara a karkashin jogirancin Hon Rt Sanusi Garba Rikiji ta dakatar da 'Yan majalisar dokokin Jihar masu goyon bayan mataimakin Gwamnan Jihar har su Gudu (4).
A zaman ta na yau Alhamis 3/1/2019 wanda Shugaban majalisar ya jagoranta, Hon. Isah Abdulmumini T/Mafara ya gabatar da kuduri na dakatar da wadannan 'Yan majalisu guda gudu (4).
Yan Majalisun sun hada da Hon. Abdullahi Muhammed Dansadau wanda shine mai tsawatarwa na majalisar kuma mai wakiltar Maru ta Kudu, sai kuma Hon. Malam Mani Masaba, Hon. Mansur Ahmad Musa Bungudu Mai wakiltar Bungudu ta Yamma tare da Hon. Salisu Musa Tsafe Kainuwa Dan Majalisa mai wakiltar Tsafe ta Gabas.
Bincike ya nuna cewa, dakatar da su bai rasa alaka da goyon bayan kugiyar nan ta G8 wadda tayi turjiya game da yunkurin Gwamnan jihar na dauki dora da ya so yayi.
Wata majiya da muka samu kuma tace Shugabannin majalisar suna jin tsoron idan Gwamna ya kawo kasafin kudi na shekarar bana a majalisar wadannan Yan majalisar suna iya kin aminta da shi.
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
GWAMNAN JIHAR ZAMFARA YA NISANTAR DA KANSA AKAN DAKATAR DA 'YAN MAJALISU HUDU DA AKAYI.
Daga Salisu Bello . Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya nisantar da kan sa da sa hannu wajen dakatar da 'yan Majalisar do...
-
A yau ne wa'adin kananan hukumomi a jihar zamfara yake cika, wanda aka masu na shekara uku kamar yadda doka ta tanada a jihar ya zamfar...
-
Ankashe mutane 18 akauykkan Jahar Zamfara ----------------- Akalla mutane goma sha takwasne 18, aka ruwaito ankashe akayukkan karamar Huku...
-
Daga... Ibrahim Bello Gusau Ibg Abun da ake tsammani a zaman kotu na yau alhamis 3-1-2019 bai wuce na bayyanar shugabar hukumar zabe...
No comments:
Post a Comment