Friday, January 4, 2019

SHIRE-SHIREN TSIGE MATAIMAKIN GWAMNAN ZAMFARA SUN KANKAMA.

Daga...
Aliyu Sani Gusau.

Dakatar da yan Majalisu 7 hadi da cewa sun karbi Naira miliyan (30m) ga wani Dan takarar Gwamnan jihar zamfara, bai rasa Nasaba da shire-shiren da ke akwai na tsige mataimakin gwamnan Zamfara Malam Ibrahim wakkala liman...
------------------------------------------------

1. Hon. Salisu Musa kainuwa Tsafe,
2. Hon. Abdullahi Mai Kano Dan sadau,
3. Hon. Dayyabu Rijiya,
4. Hon. Mansur Ahmed Bungudu,
5. Hon. Mani malam  Muminu,
6. Hon. Hashimu Gazura,
7. Hon. Abubakar Ajiya Bukuyum,

Wadannan yan majalisun Sune suka Kira taron manema labarai yau Jumu'ah a Gusau babban birnin jihar zamfara, domin bayyanawa duniya katobarar da Majalisar dokoki tayyi, karkashin jagoranci kakakin majalisar dokokin jihar zamfara da kuma bandar dake akwai kwance Kasa Na Dakatar da wasu daga cikin yan majalisar dokokin da akayi ba akan ka'ida ba,

Wayanda aka Dakatar sun hada da,

1. Hon. Salisu Musa Tsafe,
2. Hon. Mansur Bungudu,
3. Hon. Abdullahi Dan sadau,
4. Mani malam Muminu,

Mai magana a madadinsu lokacin taron Hon. Salisu kainuwa yace an dakatar dasu ne kawai akan kin amincewa da korafin Gwamna yari, akan Karin wa'adin daya nemawa shugabanin kananan hukumomi Wanda suka fadawa majalisa cewa wannan bukata ta sabawa doka.

Sannan ya Kara da cewa an dakatar dasu ne a lokacin Hutu Wanda majalisa keyi.

Kuma Babu wani kwamiti da aka kafa musu kafin dakatar dasu daga majalisar  balle su Kare kansu anyi haka ne kawai don dalilin siyasa saboda Sunce abi doka Wanda kuma shine aikin Dan majalisa.

Sanan yakara dacewa dakatar damu tabbas banan abun zai tsayawaba, saboda wannan na nuni da tsohon shirin su na cire mataimakin gwamnan Zamfara.

No comments:

Post a Comment

GWAMNAN JIHAR ZAMFARA YA NISANTAR DA KANSA AKAN DAKATAR DA 'YAN MAJALISU HUDU DA AKAYI.

Daga Salisu Bello . Gwamnan Jihar Zamfara Abdulaziz Yari Abubakar ya nisantar da kan sa da sa hannu wajen dakatar da 'yan Majalisar do...